Posts

Zango Ya sayawa Matarsa Dankareriyar Mota

Image
Fitaccen jarumin fina finan hausa Adam A Zango,  Ya yiwa Matarsa kyautar musamman da sabuwar Dankareriyar mota. Zango ya buga hoton motar kirar  Honda (Continue Discussion) a shafinsa na Instagram inda ya yi wadansu kalamai ma su cike da nuna kauna da Soyayya ga matar ta sa,  a cikin harshen turanci ga abun da yace. "Sabuwar mota kyauta ga matata,  kuma Sarauniyata "

Gabar Ali Nuhu da Zango ta Kare

Image
Ga dukkan alamu an kawo karshen duk wani tashin tashina tsakanin wadannan manyan jaruman Kannywood. Rigimar ta kare ne bayan da Adam A Zango ya fito a ranar alhamis 6 ga satumba ya wallafa sakon ban hakuri da neman Afuwa ga Ali Nuhu a shafinsa na Instagram. Shima Ali Nuhu ya wallafa wakar  Adam A Zango Akan nasa shafin,  wanda wannan ke nuni da cewa sun Shirya. Idan za ku iya tunawa an dauki tsawon shekara guda ana tafka wannan mummunan rikici da ya janyowa mutane da dama rudani da rasa abun yi.    Tuni mutane na cigaba da bayyana ra'ayoyinsu akan wannan batu.

SA'INSA TSAKANIN KISHIYOYI..KISHI NE KO KWADAYI?

Ganin yadda al'amura ke cigaba da lalacewa ne yasa ni yanke shawarar wannan rubutu don jawo hankalin 'yan uwa iyaye mata bisa wannan babbar matsalar ta kishi domin sanannen abu ne gaduk mai bibiyar kafafen yada labaru na gani ko na karatu irin yadda kullum muke cin karo da munanan labarai na cewar kishiya ta kone yar uwar zamanta da ruwan zafi ko kuma kaji kishiya ta hallaka dan yar uwar zamanta, kai hatta makonnin da suka gabata sai da jaridar aminiya ta bankado wani labarin wata mata wacce don rashin tausayi da karancin imani ta shayar dan abokiyar zamanta man fetur yaron ya sheka har lahira, to ire iren wannan matsaloli da rashin imani yana nan ya zama ruwan dare gama duniya domin ko baka mu'amala da harkokin labaru to na tabbata a unguwar dakake baza ka kasa sanin ko cin karo da kwatankwacin irin wannan matsalar ba awani gidan zaka samu ba zaman lafiya kullum cikin dambace wa ake tsakanin kishiyoyi babu zaman lafiya kullum sai rikici da gaba da juna.  To w

Sarkin Jama’are ya albarkaci wakata - Badariyya meke tsakaninta da AMINU BAGWAI HAR YAYI MATA WAKA?

“Godiya ga mutan Jama’are, Jama’are garin Badariyya!” Wakar da take ta tashe ke nan a sassan kasar nan har ma da kasashen waje. Amma wace ce Badariyya? Wakilinmu ya yi tattaki har zuwa garin Jama’are, inda ya gana da Badariyya, ta yi masa bayani filla-filla, yadda ta hadu da mawaki Aminu Bagwai, wanda kuma ya wake ta. Ga yadda tattaunawar ta kasance: Ki gabatar da kanki ga masu karatu? Sunana Badariyya A Jarma, wacce yanzu aka fi sani da Badariyya Jama’are. An haife ni a ranar 1 ga watan Maris, 1990 a Karamar Hukumar Jama’are da ke Jihar Bauchi. Ko mene ne sanadiyyar haduwarki da Aminu har ya yi maki waka? Lambar wayarsa na nema, da na samu sai na kira shi don ya yi mini karin bayani a kan wakarsa da ya yi ta ta’aziyyar wadanda suka yi hadari a jirgin ruwa, musamman da yake takaddama ta kaure a kan ko hakan ya faru ko a’a. Da na kira shi ne ya sanar da ni tabbas hakan ya faru, a nan na yi masa jaje. Daga nan sai ya tambaye ni ko ina

SHARHIN NA MUSAMMAN KAN FIM DIN MALIKA.

Sharhi kan fim xin Malika 1 da na 2 Kamfanin: Saira Movies. Labari/Tsarawa: Maje El-hajij. Manajan shiri: Sani Mai iya. Shiryawa: Nazifi Asnanic. Ba da Umarni: Aminu Saira. Shekarar fitowa: Disamba, 2011 Lokaci Malika 1: Awa 1 da minti 13 da kuma sakwan 45 Lokaci Malika 2: Awa 1 da minti 13 da sakwan 13 Yawan fitowa Malika 1: 32 Yawan Fitowa Malika 2: 26 ‘Yan wasa: Ali Nuhu, Nafisa Abdullahi, Maryam Muh’d, Rabi’u Rikadawa, Jamila Umar, Sadiq Ahmad, Hafsat Sharaxa da sauransu. Labarin Abdulmajid (Ali Nuhu), wani xan jarida mai yin aiki tsakaninsa da Allah ne da matarsa Karima (Nafisa Abdullahi), mai tsananin kishi da zurfin ciki, wanda Malika (Maryam Muh’d), mace marar kamun kai, kuma tsohuwar budurwar Abdulmajid, suka haxa kai da qanwarsa Ummi (Jamila Umar) da mijinta Alhaji Barmo (Sadiq Ahmad), wajen kunna masa wutar rikici da rashin zaman lafiya a gidansa, sakamakon rubutu da yake yi a kan Alhaji Barmo, saboda zaluncin da yake yi, rashin zaman lafiyar da har ya shafi gidan s

Lalacewar mata a Nijeriya

Image
in an ce karuwa to za ka ji jama'a suna fassara ta daban-daban. In abin ka tambaya ne, me ake nufi da karuwa? Wani zai ce maka mai zaman kanta, wani ya ce mazinaciyar da duk lokacin da aka neme ta da yin zina za ta yi. Wasu kuma na fassara wacce take gaban iyayenta, amma mai wadannan siffofi da na ambata da 'yar iska. Ma'ana a nan karuwa ita ce wacce ta bar gidansu, 'yar iska kuwa wacce take gaban iyayenta ko da aikinsu daya ne. Amma ni ina ganin da wacce ta bar gidansu da wacce akan zo a dauke ta a kai ta duk inda aka ga dama a yi zina da ita a dawo da ita gidansu da wacce za ta fita wani lokaci ta dawo in dare ya raba, wata rana ta kwana ta dawo da safe, to a nan fassarar dai shi ne karuwa ce, dukkansu aikin daya ne. In muka faro daga Legas za ka ga karuwanci a wannan jiha yana daya daga cikin manyan sana'o'i a wajen mata. Idan ka duba za ka ga mata a titi tamkar an koro su ne. Wasu a cikinsu ba su da inda za su, sun fito ne ko za su yi dace wani

Wani Dan Fulani A Banki

wani baffulatani wai zai wuce ta banki sai ya lura da yadda mutane ke saka katin ATM suna cire kudi gogan naka ba sai ya tsaya ba, yace ikon allah daga ansaka kati sai kudi ya fito? ashe ga hanyar samun kudi asauwake bamusani ba? sai yaje ya sa nasa katin sai computer ta tafi dashi ya jira yaga babu kudi ba kati sai ya fara fada akazo aka tambayeshi sai yace yasa katin sa amma ba kudi ba kati sai aka kai shi customr care suka ce wanne irin kati kasa baba, GOGAN SAI YACE YAKUKE TAMBAYA TA WANNE KATI ZAN SA IDAN BA KATIN DAN KASA BA?9(identity card).